input license here

Anyi Garkuwa Da Gawa Domin Neman Kudin Fansa!!


'Yan sanda sun kama mutum biyu da ake zargi da garkuwa da gawar wata tsohuwa a kudu maso-gabashin Najeriya.

'Yan sanda daga Oweri, babban birnin jihar Imo, sun ce mutanen sun sace gawar ne daga wajen ajiye gawa a wani asibiti, kuma suka kai ta daji suna masu neman naira miliyan hudu a matsayin kudin fansa daga asibiti da kuma iyalan marigayiyar, in ji 'yan sanda.

An kama wadanda ake zargin, wadanda a baya aka taba samu da laifi, a wani samamen da aka kai musu.

Kwanan nan aka sako mutanen daga gidan yari bayan sun yi zaman kaso bisa laifin garkuwa da mutane.
Related Posts
LastNg
Yusuf Musa By Name Iam the CEO/Founder Of www.lastng.com
SHARE

Related Posts

Subscribe to get free updates

Post a Comment

Copyright 2020 © ModernTheme

DMCA.com Protection Status